Jirgin ya fadi ne muntina shida bayan tashinsa a safiyar yau Lahadi daga birnin Addis Ababa na kasar Habasha zuwa birnin Nairobi fadar mulkin kasar Kenya.
Mahukuntan kasar Habasha sun sanar da cewa dukkanin mutanen da suke cikin jirgin sun rasa rayukansu, wadanda suka hada da 'yan kasar ta Habasha, da kuma 'yan wasu kasashe daban-daban.
Tuni Pira ministan kasar ta Habasha, Abiy Ahmed, ya aike da sakon ta'aziya ta shafinsa na twitter ga iyalen wadanda hatsarin jirgin ya yi ajalin su.